Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta sanya hawa jirgin ƙasa kyauta sabo da Kirsimeti

Gwamnatin Nijeriya ta sanya hawa jirgin ƙasa kyauta sabo da Kirsimeti

0
Gwamnatin Nijeriya ta sanya hawa jirgin ƙasa kyauta sabo da Kirsimeti

 

Gwamnatin taraiya ta sanar da cewa ƴan ƙasa za su hau jirgin ƙasa kyauta daga 24 ga watan Disambar da mu ke ciki zuwa 4 ga Janairu, 2022.

Manajan Darakta na Hukumar Kula da Harkokin Jirgin Ƙasa, Fidet Okhiria ne ya baiyana hakan a wata ganawa da ya yi da Kanfanin Daillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Juma’a a Abuja.

Ya cean ɗauki matakin ne domin saukakawa ƴan ƙasa su yi zirga-zirga a lokutan bikin Kirsimeti.

“Mu na kira ga fasinjoji da su je su karɓi sahihin tikiti a guraren da su ka dace.

“Mu na kira ga fasinjoji da su bi ƙa’idojin kariya da ga kamuwa da korona ta hanyar sanya takunkumin fuska,” in ji shi.