Home Kasuwanci Gwamnatin Taraiya na shirin tara Naira biliyan 150 da ga harajin kuɗin katin kiran waya

Gwamnatin Taraiya na shirin tara Naira biliyan 150 da ga harajin kuɗin katin kiran waya

0
Gwamnatin Taraiya na shirin tara Naira biliyan 150 da ga harajin kuɗin katin kiran waya

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya amince da karɓar kashi 5 na haraji da ga katin kiran waya, jaridar The Cable ce ta gano hakan.

Jaridar ta gano cewa harajin na ɗaya daga cikin sabbin haraje-haraje da a ka ɓullo da su a dokar kuɗaɗe ta ƙasa ta 2020 da Buhari ya rattaba hannu.

A sanarwar da The Cable ta gani, Ministar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmed, ta baiwa Hukumar Kwastan umarnin fito da wani tsari na cajar harajin a kan katin kiran waya, mitar wutar lantarki da sauran su a kan kashi 5 cikin 100.

The Cable ta kuma gano cewa gwamnatin taraiya na shirin tara a ƙalla Naira Biliyan 150 da ga harajin, inda za ta baiwa Hukumar Kwastan na’ura biliyan 10 a ciki, daidai da kashi 7 na kuɗin, a matsayin ladan karɓar harajin da ga hannun ƴan ƙasa.

Katin waya na ɗaya da ga cikin kayayyakin da a ka saka za a riƙa karɓar haraji na kashi 5, wanda a ke shigo wa da su ko kuma a nan cikin gida a ke ƙera su, shine sai a saka musu haraji a lokacin da a ke ƙera su, kamar yadda sashi na 21(1) na dokar ya tanada.