Home Kasuwanci IMF na son Nijeriya ta cire tallafi man fetur da wutar lantarki gaba ɗaya

IMF na son Nijeriya ta cire tallafi man fetur da wutar lantarki gaba ɗaya

0
IMF na son Nijeriya ta cire tallafi man fetur da wutar lantarki gaba ɗaya

 

Hukumar Ba da Lamuni ta Duniya, IMF, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta cire tallafin man fetur da na wutar lantarki gaba ɗaya a farkon shekarar baɗi.

IMF ta yi kiran ne a wani kundin sakamakon bincike da ta yi a ƙarshen ziyarar da ma’aikatanta su kawo Nijeriya, a ƙarƙashin jagorancin l Artile IV.

Hukumar ta kuma i kira da Nijeriya ta yi garambawul hidimomin kuɗaɗe, canjin kuɗaɗe, kasuwanci da tsarin mulki domin gyara matsalolin da su ke hana ƙasar ci gaba.

A sanarwar da ta fitar, IMF ta ce ya kamata a cire tallafin man fetur da na wutar lantarki domin hakan ne zai zama wani ginshiƙi na gyaran tattalin arzikin ƙasar nan.