Home Labarai Jami’ar tarayya dake Dutse a jihar Jigawa ta yaye dalibai 427

Jami’ar tarayya dake Dutse a jihar Jigawa ta yaye dalibai 427

0
Jami’ar tarayya dake Dutse a jihar Jigawa ta yaye dalibai 427

 

Hassan Y.A. Malik

Daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse, jihar Jigawa, FUD, 54 ne suka samu kammala jami’ar da digiri mai daraja ta daya.

Shugabar jami’ar, Farfesa Fatima Batul-Muktar ce ta bayyana hakan a jiya Litinin a birnin Dutse, a wani shiri na bikin yaye daliban.

Farfesa Batul, ta bayyana cewa dalibai 427 jami’ar ta yaye a bangarorin ilimai daban-daban a bana, kuma a cikinsu, guda 54 sun kammala da digiri mai daraja ta daya, 223 kuma da digiri mai daraja ta biyu, sai 149 kuma da digiri mai daraja ta uku, inda dalibi 1 tilo ya gama da digiri mai darajar da kyar na sha.

Shugabar ta ci gaba da cewa, tun bayan bude makarantar a shekarar 2011, jami’ar ta ci gaba da samun nasarori ta bangaren harkokin koyo da koyarwa da ma samar da gine-ginen azuzuwa, dakunan karatu da ofisoshin ma’aikata da kuma kirkirar sababbin tsangayoyi.

“Mun fara ne da tsangayoyi 5 kacal a shekarar karatu ta 2011/2012, amma zuwa yanzu makaratar na da tsangayu 19 kuma adadin dalibai ya tashi daga 202 a sheakarar budewa zuwa 5,963 a halin yanzu.”

Farfesa Batul ta ci gaba da cewa, yana cikin tsare-tsaren da hukumar jami’ar ke yi na bude wata sabuwar tsangaya ta ilimin gudanarwar rayuwar dan adam da dabi’unsa, wanda za a fara karatu a tsangayar a watan Satumba mai zuwa.

Zuwa sheakarar 2019 kuma, jami’ar za ta bude tsangayar karantar da ilimi matakin farko don ta bada nata gudunmawar wajen horar da malamai a kasar nan.