Home Labarai Jam’iyyu 46 sun ayyana Atiku a matsayin dan takararsu na Shugaban kasa

Jam’iyyu 46 sun ayyana Atiku a matsayin dan takararsu na Shugaban kasa

0
Jam’iyyu 46 sun ayyana Atiku a matsayin dan takararsu na Shugaban kasa

Gamayyar jam’iyyun hamayya 46 ne da suka hada da babbar jam’iyyar hamayya ta PDP suka ayyana Atiku Abubakar a matsayin dan takararsu na Shugaban kasa a zaben 2029.

Shugaban gamayyar kuma tsohon Gwamnan jihar Osun Olagunsoye Oyinlola ne ya bayyana hakan a babban birnin tarayya Abuja a lokacin da gamayyar jam’iyyun suka yi babban taronsu.

Jam’iyyun da suka zabi Atiku a matsayin dan takararsu sun hada da AA da DPC da MAJA da PANDEL da LP da MPN da ADC da AGAP da PPP da sauransu.