Home Labarai Jigon APC a Kaduna Isa Ashiru Kudan ya fice daga jam’iyyar

Jigon APC a Kaduna Isa Ashiru Kudan ya fice daga jam’iyyar

0
Jigon APC a Kaduna Isa Ashiru Kudan ya fice daga jam’iyyar

Wani jigo a jam’iyyar APC reshen jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan ya ajiye takardun zamansa dan jam’iyyar APC a jihar,inda ya sa kafa ya tsallake.

DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewar, Isa Ashiru wanda tohon dan jam’iyyar PDP ne, wanda kuma ya taba zama dan majalisar dokokin jihar Kaduna au biyu, kuma dan majalisar wakilai ta kasa sau biyu.

Alhaji Isa Ashiru ya aike da wasikar ficewarsa daga jam’iyyar ne zuwa ga shugaban mazabarsa ta Kudan a yankin karamar hukumar Kudan, inda ya bayar da dalilin rashin demokaradiyya a cikin gida jam’iyyar.

Ya kara da cewar shi da magoya bayansa an ware u daga cikin jam’iyyar ba’a yin komai da su, bayan kuwa da goyon bayansu ne jam’iyyar ta kai gaci a jihar ta Kaduna. Shi dai Isa Ashiru shi ne mutumin da Gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai ya kayar a zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka yi a shekarar 2014.