
Daga Hassan Y.A. Malik
Rundunar ‘yan sanda jihar Kebbi ta tabbatar da cewa an saki babban limamin garin Sanchi, Alhaji Maude Sanchi da wasu masu garkuwa da mutane suka sace.
Kamfanin dillanci Labarai ya rawaito cewa an sace Alhaji Maude ne a ranar 18 ga watan Maris.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ibrahim Kabiru ne ya bayar da tabbacin sakin Alhaji Maude a yau Lahadi a yayin da ya ke yin wani jawabi ga manema labarai da aka kira don a sanar da su batun sakin na Alhaji Maude.
“Babban limamin na cikin koshin lafiya kuma tuni ya koma cikin iyalinsa,” inji kwamishina ‘yan sanda.