Home Labarai Mai faɗar “Dan Kashiful Gummati” a wajen tafsirin Isa Waziri a Kano ya rasu

Mai faɗar “Dan Kashiful Gummati” a wajen tafsirin Isa Waziri a Kano ya rasu

0
Mai faɗar “Dan Kashiful Gummati” a wajen tafsirin Isa Waziri a Kano ya rasu

 

Alhaji Kabiru Usman Sanka ya rasu a yau talata.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Usman ya rasu bayan wata rashin lafiya da har yanzu ba a kai ga baiyana ta ba.

Kafin rasuwarsa, muryar marigayin sananna ce a gidajen rediyon Kano ga ma’abota jin fitaccen karatun tafsirin alƙur’ani mai girma na Marigayi Sheikh Isa Waziri.

Muryar marigayin ta yi suna, musamman a shekaru sama da ashirin da su ka gabata sakamakon yadda ya ke yawan faɗin “Allah Ya saka da alkhairi, dan Kashiful Gummati”.