Home Labarai Ɗan majalisar dokokin jihar Legas ya rasu a wajen ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen Tinubu

Ɗan majalisar dokokin jihar Legas ya rasu a wajen ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen Tinubu

0
Ɗan majalisar dokokin jihar Legas ya rasu a wajen ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen Tinubu

 

Ɗan majalisar dokokin jihar Legas, Abdulsobur Olayiwola Olawale ya rasu.

Ɗan majalisar, wanda aka fi sani da Omititi, shi ne wakilin mazaɓar Mushin II a jihar ta Legas

Rahotanni sun ce ɗan majalisar ya yanke jiki ya faɗi, ya kuma rasu a filin wasa na Rawang Pam Township da ke Jos, a jiya Talata.

Ya rasu yana da shekaru 60 a duniya.

Omititi ya kasance shugaban kwamitin majalisar akan ayyuka na kananan hukumomi.

A jiya ne dai ɗan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya kaddamar da yakin neman zabensa na 2023 a jihar Plateau.