
Ministar harkokin mata da iyali Hajiya Aisha Jummai Alhassan wadda aka fi Sani da Maman Taraba ta ajiye aikinta a matsayin ministar harkokin mata sannan kuma ta fice daga cikin jam’iyyar APC.
Ta bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ta aikewa Shugaba Muhammadu Buhari da jam’iyyar ta APC.