Home Kanun Labarai Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osibanjo ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba

Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osibanjo ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba

0
Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osibanjo ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba
Na farko daga hagu, Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osibanjo, sai Abba Kyari sai kuma ta farko daga dama Shugabar ma'aikatan Gwamnatin tarayya Winifred Ayo-Ita

Mataimakin Shugaban kasa, farfesa Yemi Osinbajo shi ne ya jagoranci zaman majalisar zartawar na mako-mako da ake gudanarwa a wannan Larabar a fadar Shugaban kasa dake birnin tarayya Abuja.

An fara zaman ne da misalin karfe 10:55 na safiyar Laraba. Zaman dai ya samu halartar Ministoci kamar su Lai Mohammed Minsitan yada labarai da al’adu, Minsitan kimiyya da fasaha, Ogbonnaya Onu.

Sauran su ne, Minsitan ciniki da masana’antu da zuba jari, Okechukwu Enalema; Harkokin Noma, Audu Ogbe; Ministar Mata, Jummai Alhassan da kuma karamar ministar harkokin kasashen waje, Khadija Abba-Ibrahim.

Ragowar su ne, ministar kudi, Kemi Adeosun; da karamin ministan zirga zirgar jiragen sama, Hadi Sirika, wadannan da ma wasu, sune wadan da suka samu damar halartar zaman majalisar na yau laraba a fadar Shugaban kasa.

Haka kuma, daga cikin wadan da suka halarci zaman akwai Magatakardar Gwamnatin tarayya Boss Gida Mustapha, Shugaban ma’aikatan fadar Shugaban kasa Alhaji Abba Kyari da sauransu.