Home Labarai NLC ta buƙaci a janye ƙarin farashin litar man fetur

NLC ta buƙaci a janye ƙarin farashin litar man fetur

0
NLC ta buƙaci a janye ƙarin farashin litar man fetur

Shugaban Kungiyar Ƙwadago ta Ƙasa, Joe Ajaero ya yi kira ga gwamnatin taraiya da ta gaggauta janye ƙarin farashin litar man fetur da ta yi a jiya Laraba.

A jiya ne dai kanfanin mai na kasa, NNPCL, ya sanar da karin farashin litar mai daga Naira 898 zuwa sama da Naira 1,000 a fadin ƙasar, lamarin da ya jefa yan kasar cikin damuwa.

Sai dai kuma Daily Trust ta rawaito cewa Ajaero, a wata sanarwa da ya fitar a juya Laraba ya ce gwamnatin na ta kara farashin mai a duk wata yayin da ta gaza ƙaddamar da sabon mafi ƙarancin albashi.

Hakazalika, a cewar sa, yanzu an bar kamfanonin mai masu zaman kansu su rika sayar da mai a farashin da su ka ga dama.