Home Wasanni Ranar Asabar aka buɗe Gasar Firimiya ta Najeriya

Ranar Asabar aka buɗe Gasar Firimiya ta Najeriya

0
Ranar Asabar aka buɗe Gasar Firimiya ta Najeriya

Daga Abba Ibrahim Wada Gwale

A ranar Asabar za’a fara buga gasar firimiya ta qasa bayan tafiya hutun kusan watanni uku, qungiyar qwallon qafa ta Plateau United c eta lashe gasar da aka kammala a watan Nuwamban shekarar data gabata.

Qungiyar qwallon qafa ta Kano Pillars zata fara kece raini da qungiyar qwallon qafa ta Katsina United a garin Katsina a ranar Asabar din yayinda mai kare kambu Plateau zata kai ziyara Nasarawa United domin fara kambunta.

Qungiyar qwallon qafa ta Abia Warriors wadda mai koyarwa Rafael Everton, dan qasar Brazil yake jagoranta zata kece raini da wadda ta qare a mataki na biyu a gasar data gabata wato MFM.

El-kanemi ta qasar Maiduguri zata kai ziyara jihar Rivers domin fafatawa da qungiyar qwallon qafa ta River United yayinda qungiyar Heartland ta jihar Imo wadda ta hawo gasar wannan shekarar zata karbi baquncin Sunshines Stars na garin Akure.

Gayadda wasannin zasu kasance a satin wasa na farko

Kwara United  vs  Niger Tornadors

FC Ifeanyi Uba  vs  Yobe Desert Stars

Wikki Tourists  vs  Go- Round FC

Akwa United  vs  Rangers International

Lobi Stars  vs  Enyimba International

Heatland  vs  Sunshine Stars FC

Katsina United  vs  Kano Pillars

Nasarawa United  vs  Plateau United

Rivers United  vs  El-Kanemi Warriors

Abia Warriors  vs  MFM FC

Za’a buga wasannin a ranakun yau Asabar da kuma gobe Lahadi a filayen wasanni daba-daban dake fadin tarayyar qasar nan.