Home Labarai Rashin tsaro: Ƴan Nijeriya 11,500 ne su ka tsere zuwa Nijar a Nuwamba- UNHCR

Rashin tsaro: Ƴan Nijeriya 11,500 ne su ka tsere zuwa Nijar a Nuwamba- UNHCR

0
Rashin tsaro: Ƴan Nijeriya 11,500 ne su ka tsere zuwa Nijar a Nuwamba- UNHCR

 

Ma’aikatar kula da ƴan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin-Duniya, UNCHR ta baiyana cewa rashin tsaro a arewa-Maso-Yammacin Nijeriya ya tilastawa mutane 11,500 gudun hijira zuwa Ƙasar Nijar a watan Nuwamba.

Kakakin UNCHR, Boris Cheshirkov ne ya baiyana haka a wata ganawa da manema labarai a Geneva a yau Juma’a.

Ya ce ” mu na cikin damuwa da tashin hankalin da ke faruwa a arewa-Maso-Yammacin Nijeriya kuma yanayi ne da ya ke buƙatar haɗa hannu guda wajen samar da zaman lafiya.

“Yawancin sabbin zuwan sun samu matsuguni a ƙauyuka 26 a cikin Nijar ɗin. Yawancin ƴan gudun hijirar mata ne da ƙananan yara. Saboda haka muna buƙatar taimako mai ƙarfi domin sauƙaƙa rayuwar al’umma,”