Home Kanun Labarai An sake sanya zare tsakanin Hameed Ali da ‘yan Majalisar Dattawa

An sake sanya zare tsakanin Hameed Ali da ‘yan Majalisar Dattawa

0
An sake sanya zare tsakanin Hameed Ali da ‘yan Majalisar Dattawa
Shuggaban hukumar Kwastam ta kasa, kanarHameed Ali mai ritaya

Sa-toka sa-katse tsakanin Shugaban hukumar Kwasttam ta kasa Kanar Hameed Ali mai ritaya da ‘yan majalisar dattawa, har yanzu bata kare ba. A ranar litinin din nan, akai musayar yawu sakanin Hameed Ali da ‘yan majalisar dattawan.

Wannan sabani ya biyo bayan wata ziyara da kwamitin musamman kan sharar masana’antu na majalisar dattawa ya kai shalkwatar hukumar kwastam ta kasa a birnin tarayya Abuja.

Shugaban kwamitin, Sanata Dino Melaye, mun yi tsammanin Shugaban hukumar kwastam din zai tsaya dan ya karbi tawagar Sanatacin a harabar hukumar, ba kawai muje mu jira shi a dakin taro na hukumar ba.

Yace wannan shi ne tsarin da ake bi,idan baki sun shigo Shugaban hukumar ya fito domin ya karbe su, a ko ina, yace amma abinda Hameed Alin yayiwa Kwamiin abu ne da sam bai dace ba, kuma ya karya tsari.

“Kaafin na karanta jawabin wannan kwamiti da yake gabana, bari nayi wata magana kan abinda akai mana yayin da muka shigo gidannan na karya tsari da ka’ida”

“Shugaban Kwastam, maimakon ka zo ka nan dakin taro ka same mu, ya kamata ace kaine da kanka ka fito harabar hukumar nan ka tarbemu ka yi mana barka da zuwa” A cewar Dino Melaye.

A lokacin da yake mayar da martani kan wannan korafi, Shugaban hukumar Kwastam ta kasa hameed Ali, ya shaidawa ‘yan majalisar cewar, hukumar Kwastam na da nata tsarin, sabanin wanda aka sani ana yi a gurare da ban daban, ba kuma dole ne sai Kwastam tayi koyi da abinda wasu ke yi ba.

“Muna da tsare tsare irin namu, na yaddamuke karbar baki kamarku. Babu bukatar sai na sauko daga ofishina a sama na zo kasa dan na karbe ku, kamar yadda babu wani sanata da ya taba saukowa daga ofishinsa domin ya karbemu idan mun je majalisar dattawa”

“Bari na sake tabbatar muku da cewar, mu a hukumar Kwastam, muna yiwa al’ummar kasa aiki ne. Mun aminta da tsarin kasarmu, muna aiki da juna domin ciyar da ita gaba ba tare da tunanin zamu sabawa wani ko baiwa wani haushi, ba mu fatanmu muyi abinda ya dace ko da wani bai ji dadi ba” Inji Hameed Ali.

NAN