Home Labarai An saki Dino Melaye, ya soke tafiyarsa zuwa kasar Moroko

An saki Dino Melaye, ya soke tafiyarsa zuwa kasar Moroko

0
An saki Dino Melaye, ya soke tafiyarsa zuwa kasar Moroko

Sanata Dino Melaye dan majalisar dattawa mai wakiltar jihar Kogi ta yamma, wanda jami’an hukumar kula da shige da fice ta kasa suka kama ranar Litinin a filin sauka da tashin jiragen sama na Abuja, ya samu ‘yanci, inda aka sake shi bayan da ya shafe sa’o’i biyu a hannun jami’an NIS.

Mai magana da yawun Sanatan, Gideon Ayodele ya tabbatar da cewar an saki mai gidan nasa, bayan da aka tsare shi dazu da safe a filin jirgin saman Abuja,akan hanyarsa ta zuwa kasar Maroko.