
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya Isa Maiduhuri babban birnin jihar Borno domin duba sojojin Najeriya da suka jikkata da kuma jajanta musu kan harin da ‘yan Boko Haram suka kai a garin Metele inda suka kashe sojoji sama da dari.
Wannan harin da Boko Haram suka kai a garin na Metele ya tayar da Kura sosai a Najeriya. Indai akai ta dora laifin alhakin wannan harin akan shugabannin sojojin Najeriya dake jihar Borno.