
A ranar Juma’a Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Shugabanni da mambobin hukumomin Gwamnati da aka jima ana tsumayin fitar sunayen.
Wata sanarwa da ta fito daga ofishin Sakataren Gwamnatin tarayya, tana cewar, Shugaba Buhari ya amince da nadin mutum 209 a matsayin Shugabannin hukumomin Gwamnati daban daban, da kuma mambobi guda 1,258.