Home Labarai Shugaba mai tsoron Allah ba zai iya yaki da cin hanci ba a Najeriya – Bishop Kukah

Shugaba mai tsoron Allah ba zai iya yaki da cin hanci ba a Najeriya – Bishop Kukah

0
Shugaba mai tsoron Allah ba zai iya yaki da cin hanci ba a Najeriya – Bishop Kukah
Bishop Matthew Kukah

Babban Bishop na Sakkwato, Rabaran Matthew Hassan Kukah, a ranar laraba, ya bayyana cewar, yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya, wani babban al’amari ne da yake bukatar ba wai kawai mutum mai tsoron Allah ba.

Mista Kukah yana bayyana haka ne a wajen bikin kaddamar da wani littafi mai suna “The Shadow List” wanda cibiyar yada bayanai da harkar jarida ta Afurka ta shirya a babban birnin tarayya Abuja.

“Kawar da cin hanci da rashawa, tare da gina sabuwar al’umma da ba tada sofane na cin hanci, ba batu bane kawai na muna fata. Wannan batu ne da yake bukatar jajirtaccen Shugaba ba wai kawai mai tsoron Allah ba”

“Na sha nanata cewar, Najeriya baata bukatar Shugaba mai tsoron Allah, domin mai tsoron Allah sau da dama yakan zama uzuri. Idan kana bukatar tsoron Allah to kana iya zama mai tsoron Allah in kaso”

Mista Kukah, yaga baiken masu mulki inda yace sun zama tamkar wani gungugu na masu laifi, domin kowa ka daga shi sai ka tarar da kwance yake cikin dukiyar haram.

Kukah yace, idan muka tsaya muka fahimci zahirin abinda yake damun kasarmu, to mun taimaki kanmu.

Yace,ina mamakin yadda ‘yan Najeriya a koda yaushe suke murna idan an samu sabuwar Gwamnati, wanda daga baya sai ka samu sabuwar Gwamnatin ba ta da maraba da wadan da suka gabace ta.

“Babu wanda yayi zaton shekaru ukun nan da suka wuce, zamu kasance a yadda muke ciki yanzu”

A lokacin da yake tofa albarkacin bakinsa, tsohon Shugaban hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, Malam Nuhu Ribadu, ya jinjinawa mawallafin littafin, a bisa yadda ya dauki lokaci yana bayanin akan Najeriya da kuma batun yaki da cin hanci da rashawa.

Ribadu ya bayyana gamsuwarsa da kaddamar da irin wadannan litattafai, domin a cewarsa zai taimakawa masu karantawa fahimtar yadda Najeriya ta sanya gaba kan batun yaki da cin hanci da rashawa.

Mahalarta taron da yawa da suka tofa albarkacin bakinsu sun jinjinawa mawallafin littafin a kokarin na bayyanawa ‘yan Najeriya halin da ake ciki kan batun yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya.