
Shugaban jam’iyyar APC na Kasa Uche Secondus ya ragargaji tsohon Ministan Ilimi kuma Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau kan batun ficewarsa daga PDP zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta APC.
Secondus ya bayyana cewar daman can Shekarau na tattaunawa da mutanan APC domin komawarsa jam’iyyar. Yace duk korafin da Shekarau yake yi akansa sam ba gaskiya bane.
A cewarsa yayi iyakar kokarinsa wajen ganin an sasanta al’amura a jihar Kani amma Shekarau ya toshe dukkan wata kofar tattaunawa da shi.
Mista Secondus ya bayyana hakan je ya hannun mai magana da yawunsa.