Home Labarai DA ƊUMI-ƊUMI: Kotu ta kori ƙarar hana rantsar da Tinubu tare da cin tarar mai ƙarar Naira miliyan 15

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotu ta kori ƙarar hana rantsar da Tinubu tare da cin tarar mai ƙarar Naira miliyan 15

0
DA ƊUMI-ƊUMI: Kotu ta kori ƙarar hana rantsar da Tinubu tare da cin tarar mai ƙarar Naira miliyan 15

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da ke neman a dakatar da rantsar da Bola Tinubu, dan takarar jam’iyyar APC a matsayin shugaban ƙasa.

Da kuri’u 8,794,726, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/ 657/2023, masu shigar da kara – Godiya Isaiah, Paul Audu da Anongu Moses – sun yi zargin cewa Tinubu ya yi karya a cikin form dinsa na EC9 cewa shi ba dan wata kasa ba ne.

Sun kuma yi zargin cewa zababben shugaban ya yi karya a kan rantsuwar shekarunsa.