Home Labarai Yajin aikin ASUU: Gobe za mu datse tituna a Oyo — Ɗalibai

Yajin aikin ASUU: Gobe za mu datse tituna a Oyo — Ɗalibai

0
Yajin aikin ASUU: Gobe za mu datse tituna a Oyo — Ɗalibai

 

Ɗalibai, ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Ɗalibai ta Ƙasa, NANS sun yi barazanar cewa za su datse duk wasu titunan gwamnatin taraiya a Jihar Oyo da ga gobe Talata idan har Ƙungiyar Malaman Jami’a, ASUU ta ci gaba da yajin aiki.

Wani ɓangare na ƙungiyar da ga rukunin B ne su ka yi baraza 44nar.

Sun baiyana hakan ne yayin da su ke tsaka da zanga-zanga a sakatariyar NUJ da ke Iyangu, a Ibadan.

Ƙungiyar, wacce ta ke ƙarƙashin shugabancin Steven Tegbe ya baiwa gwamnatin taraiya da ASUU shawarar su sasanta a tsakanin su.

Ya ce babu wata bukatar a yi yajin aikin tun farko idan har za a riƙa samun fahimtar juna.

Ya nuna damuwa cewa duk sanda Gwamnati da ASUU su ka samu matsala to ɗalibai ne su ne ke shan wahala.