
Yan Majalisar Wakilai ta Tarayya na jam’iyyar adawa ta PDP sun canja sheka zuwa jam’iyyar dake mulki ta APC.
Ɗan majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Birnin Abuja da Buari, Mista Zaphaniah Gisalo da wani mamba daga Jihar Kogi mai suna Yusuf Tijani ne suka yi canjin jam’iyyar.
Duk da cewa sauran ‘yan majalisun PDP sun soki lamirin wannan canja sheka, amma Jisalo da Tijani sun yi kunnen uwar shegu.