Home Labarai ‘Yan sanda sun sake gurfanar da Dino a gaban kotun Abuja

‘Yan sanda sun sake gurfanar da Dino a gaban kotun Abuja

0
‘Yan sanda sun sake gurfanar da Dino a gaban kotun Abuja

Daga Hassan Y.A. Malik

Hukumar ‘yan sandan Nijeriya ta maka Sanata Dino Melaye a gaban wata kotun majistare mai zamanta a Wuse 2, Abuja.

Sanatan da a halin yanzu ke karbar kulawa daga jami’an lafiya na babban asibin tarayya da ke birnin Abuja sakamakon tsalle da ya yi ya diro daga motar ‘yan sanda a makon da ya gabata, an kawo shi gaba alkalin majistaren a kan gadon asibiti.

‘Yan sandan sun gurfanar da Dino ne  bisa zarginsa da hannu a aikata mugun laifi

Zuwa lokacin da muka hada wannan rahoto, kotu ta ki baiwa ‘yan jarida damar shiga dakin shari’ar.

Za mu kawo yadda ta kaya…