Home Kanun Labarai ‘Yan sanda sun tabbatar da fashewar Bom a gidan Shugaban Ohaneze a Enugu

‘Yan sanda sun tabbatar da fashewar Bom a gidan Shugaban Ohaneze a Enugu

0
‘Yan sanda sun tabbatar da fashewar Bom a gidan Shugaban Ohaneze a Enugu

Rundunar ‘yan sandan jihar Enugu ta tabbatar da fashewar Bom a yankin Ukehe a gidan Nnia Nwodo, Shugaban kungiyar Ohaneze Ndigbo, kungiyar dake fafutikar kare ‘yan kabilar Igbo ta Inyamurai zalla da sanyin safiyar Lahadi.

A sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Enugu, Ebere Amaraizu ya ce, tuni kwamishinan ‘yan sandan jihar ya ziyarci yankin da fashewar Bom din ta aukua Ukehe dake yankin karamar hukumar Igboetiti a jihar Enugu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Dan Mallam Muhammad, ya sha alwashin sanya kafar wando daya da duk wadan da suke da hannu wajen tashi wannan bom din a jihar ta Enugu.

Ya kuma sha alwashin ganin an bibiya tare da kamo wadan da suke da hannu wajen tayar da wannan Bom a gidan Shugaban kungiyar Ohaneze Ndigbo, kungiyar dake fafutikar kare Inyamura zalla.