Home Ƙasashen waje An yanke wa ɗan gudun hijirar Afghanistan hukuncin kisa bisa kisan malamai 2 a Iran

An yanke wa ɗan gudun hijirar Afghanistan hukuncin kisa bisa kisan malamai 2 a Iran

0
An yanke wa ɗan gudun hijirar Afghanistan hukuncin kisa bisa kisan malamai 2 a Iran

 

 

 

A yau litinin ne aka zartar da hukuncin kisa kan wani ɗan gudun hijira ɗan ƙasar Afganistan a Iran bisa laifin kisan wasu malaman Shi’a guda biyu a farkon wannan shekarar.

An rataye matashin mai shekaru 21 a gidan yarin Vakilabad da ke arewa maso gabashin birnin Mashhad, kamar yadda shugaban hukumar shari’a ta yankin ya sanar, a cewar kafar yaɗa labarai ta Misan.

Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na cewa, laifin ya kuma faru ne a birnin Mashhad da a ke yin ibadar ta musamman a hubbaren Imam Reza na Shi’a.

Akwai kuma wasu masu laifin guda shida. Mutum na uku da aka kashe ya samu munanan raunuka a harin.

An ce harin na da alaka da addini.

Shi’a Musulunci shi ne addinin gwamnati a Iran. An samu rarrabuwar kawuna tsakanin ‘yan Sunni da ‘yan Shi’a a Musulunci, kuma sau da yawa ana samun sabani a tsakanin su.

A cewar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, akwai kusan ‘yan gudun hijira miliyan biyu da ba su yi rajista ba daga Afghanistan da ke zaune a Iran.

A cewar Iran, adadin ya haura sosai.