Home Labarai YANZU-YANZU: Sarkin Musulmi ya tabbatar da ganin watan Ramadan a Nijeriya

YANZU-YANZU: Sarkin Musulmi ya tabbatar da ganin watan Ramadan a Nijeriya

0
YANZU-YANZU: Sarkin Musulmi ya tabbatar da ganin watan Ramadan a Nijeriya

 

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sultan Sa’ad Abubakar, ya tabbatar da ganin jaririn wata, inda hakan ya nuna cewa gobe Asabar, 2 ga watan Afrilu, za ta zama 1 ga watan Ramadan.

A jawabin ganin watan a kafafen yaɗa labarai kai tsaye, Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya ce Sultan ɗin ya tabbatar da ganin jinjirin watan a wasu garuruwa a nan Nijeriya.

Sarkin Kano ya ce Sultan ya tabbatar da ganin watan a garin Bajoga da ke Jihar Gombe, Kauran Namoda a Jihar Zamfara da sauran jihohi.

Ya ce bayan wannan tabbatar wa, Musulmai za su tashi da azumi, inda watan Ramadan ya zama kwana 1 kenan a goben.

Bayero ya kuma hori al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan dama su yi wa ƙasa addu’a.