Home Kanun Labarai Yanzu-yanzu: An shawarci ASUU da Gwamnatin Tarayya da su sulhunta a wajen kotu

Yanzu-yanzu: An shawarci ASUU da Gwamnatin Tarayya da su sulhunta a wajen kotu

0
Yanzu-yanzu: An shawarci ASUU da Gwamnatin Tarayya da su sulhunta a wajen kotu

 

 

Kotun daukaka ƙara da ke Abuja ta buƙaci kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da gwamnatin tarayya da su bi hanyar yin sulhu a wajen kotu domin magance kai-ruwa-ranar da su ke ta yi  tsakanin su.

Kotun ta dauki wannan mataki ne a yau Laraba yayin da ta ke sauraron karar da kungiyar ASUU ta shigar kan hukuncin da kotun masana’antu ta kasa ta yanke a ranar 21 ga watan Satumba, inda ta umarci malaman jami’o’in da su dakatar da yajin aikin da suke yi.

Cikakken bayani na nan tafe…