Home Labarai YANZU-YANZU: Shugaban jam’iyyar PDP na Zamfara ya rasu

YANZU-YANZU: Shugaban jam’iyyar PDP na Zamfara ya rasu

0
YANZU-YANZU: Shugaban jam’iyyar PDP na Zamfara ya rasu

 

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar Zamfara, Ahmad Sani Kaura ya rasu.

Rahotanni sun bayyana cewa ya faɗi ne ya rasu a na tsaka da taro da kungiyar malaman addini a yau Laraba a Gusau.

Wani kusa a jam’iyyar, Aminu Umar ya ce dama marigayin bashi da lafiya, kuma bai warke ba lokacin da ya halarci taron.