Home Nishaɗi ’Yar Sarkin Kano ta samu juna biyu

’Yar Sarkin Kano ta samu juna biyu

0
’Yar Sarkin Kano ta samu juna biyu
Fulani Siddika

Daga Bashir Muhammad

Hoton Fulani Siddiƙa, wacce ɗiyar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi (Nabiyu) ce, ya ɓulla a kafar sada zumunta ta Instagram da ƙwaryar ciki.

Siddika da angonta Umar Kurfi

An sha shagulgulan biki a birnin Kano yayin da Fulani Siddiƙa ta auri angonta Umar Kurfi a ranar 23 ga watan Disambar bara.

Hoton wanda kamfanin dauƙar hoto na Atilary Photography ke terere da shi a Internet, ya ja hankalin akasarin mutane zuwa tofa albarkacin bakinsu.

A yayin da wasu ke ganin hoton ya saɓawa ƙa’idar addini, wasu kuma sai sambarka su ke yi Siddiƙa ta yi nauyi.

Sarki Sanusi (Nabiyu) ya kawo zamananci da dama a harkar masaurar Kano. A watannin da su ka gabata an yi ta kace-nace bayan ya tura ’yarsa ta wakilce shi babu lulluɓi a wani taro a Habuja.

Haka zalika an yi ta cece-kuce kwanan baya lokacin da sarkin ya ce ‘yar sa ta tsinkawa mijinta mari duk lokacin da ya sake ya mare ta.

Mene ne ra’ayinku akan wannan hoton?