Home Labarai Zamu rabawa ‘yan Najeriya kudaden da Abacha ya sata – Buhari

Zamu rabawa ‘yan Najeriya kudaden da Abacha ya sata – Buhari

0
Zamu rabawa ‘yan Najeriya kudaden da Abacha ya sata – Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin ya bayyana cewar za’a rabawa ‘yan Najeriya dala miliyan 320 kudaden da Abacha ya sata ya boye a kasashen waje lokacin da yake Shugaban kasa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a taron karawa una sani na kasashen rainon Ingila reshen Afurka akan yaki da cin hanci da rashawa da yiwa tattalin arziki ta’annati dake gudana a ABuja babban birnin Najeriya.

SHugaban wanda mataimakinsa Yemi Osibanjo ya wakilta, Buhari ya bayyana cewarwannan shi ne sharadin da kasar Suwizalan ta bayar yayin da take danka kudin ga Najeriya.