
Daga Mustapha Usman
‘Yar gwamnan Kano Adbullahi Umar Ganduje, wato Fatima Ganduje, ta kafe tsayin daka sai ta auri dan gidan gwamnan Jihar Oyo mai suna Idris Abiola Ajimobi.
Fatima wacce ta gama karatun ta na digiri a Jami’ar ABTI da ke Yola, ta yi nisa cikin soyayya da wannan saurayi, duk da cewa auren bai gamsar da iyayenta ba.
A cewar wani makusancin gidan Gwamna Ganduje, “an sha kwace wayoyinta a tsare ta a gida, amma duk da haka sai ta san yanda ta yi su ka yi magana ko su ka hadu.”
Shaukin soyayyar wannan saurayi da budurwarsa ya fito fili karara, yayin da ta sanya hotonsa a shanfinta na Instagram (fateeganduje) a ranar 19 ga Satumbar wannan shekarar ta na nuna wa duniya cewa Idi fa kyautar ubangiji ne a gareta.
Shi ma kuma Idris ya sanya hoton bidiyonsa tare da Fatima suna zantawa.